Amurka da Iran za su Tattauna a Oman kan Shirin Nukiliya

Amurka da Iran za su yi tattaunawa kai-tsaye a karon farko cikin wata takwas, yayin da Washington ke neman daƙile shirin nukiliyar Tehran.

Shugaba Trump ya yi barazanar daukar matakin soja idan ba a samu wata mafitar diflomasiyya ba. Wakilli na musamman na Amurka Steve Witkoff, da ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ne ke halartar ganawar da za a yi a Oman.

Iran ta ce ba laifi idan an nemi a tattauna kan rage tasirin shirinta na Nukila, amma duk wani batu na neman ta daina kera makamai masu linzami, da daina goyon bayan kungiyoyin yan gwagwarmaya a gabas ta tsakiya tamkar tsallaka jan layi ne a gareta.

Post a Comment

Previous Post Next Post