UEFA ta yi Barazanar Kaurace wa Gasar FIFA

Hukumar Kwallon Kafa ta Turai (UEFA) da ƙungiyoyin kwallon kafa 55 da ke ƙarƙashinta sun yi watsi baki ɗaya da shirin FIFA na bai wa masu zuba jari masu zaman kansu damar mallakar hannun jari a Gasar Cin Kofin Duniya da sauran manyan gasa na duniya.

UEFA ta yi gargadin cewa ƙasashen Turai za su kaurace wa duk wata gasa ta FIFA idan aka ci gaba da wannan shiri.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Alhamis, UEFA ta bayyana shirin a matsayin yunƙurin mayar da babbar gasar kwallon kafa ta duniya ta zama hanyar kasuwanci, tana mai jaddada cewa “ba a sayar da Gasar Cin Kofin Duniya.”

Hukumar ta zargi FIFA da tsara shirin a ɓoye tare da ƙoƙarin amincewa da shi ba tare da cikakkiyar tattaunawa da masu ruwa da tsaki da ke kula da harkokin kwallon kafa ba.

“Ba za a iya ɗaukar Gasar Cin Kofin Duniya a matsayin kayan saka hannun jari ba. Tana daga cikin manyan gadon wasanni na kwallon kafa, wanda aka gina tsawon ƙarni ta hanyar ‘yan wasa, ƙungiyoyin ƙasashe da magoya baya a dukkan nahiyoyi.

“Babu wani ɓangare na gasar da ya kamata a miƙa wa masu zuba jari masu zaman kansu. Ba a sayar da Gasar Cin Kofin Duniya,” in ji sanarwar.

UEFA ta kuma soki tsarin yanke shawarar FIFA, tana cewa ba shi da alhaki kuma ba za a iya kare shi ba, domin an tsara wannan gagarumin shiri a ɓoye har ya kusa samun amincewa ba tare da tattaunawa ta gaskiya da waɗanda aka ɗora wa alhakin kula da wasan ba.

Hukumar ta ce ana matsa wa ƙungiyoyin kwallon kafa na ƙasashe su amince da shirin, tana bayyana tsarin a matsayin “mulki ta hanyar tsoratarwa” maimakon yanke hukunci cikin dimokuraɗiyya.

UEFA ta bayyana cewa idan aka bai wa masu zuba jari damar mallakar hannun jari a gasannin FIFA, hakan zai sauya alkiblar kwallon kafa daga fifita muradun wasanni zuwa fifita ribar masu hannun jari.

“Da zarar masu zuba jari na waje sun mallaki hannun jari a gasannin FIFA, kwallon kafa za ta sauya har abada. Samun riba zai zama wajibi na dindindin, kuma buƙatun masu zuba jari za su rinjayi yanke duk wata muhimmiyar shawara,” in ji sanarwar.

Hukumar ta ƙara da cewa makomar kwallon kafa ba za ta kasance ƙarƙashin waɗanda babban aikinsu shi ne ƙara yawan ribar kuɗi ba, tana mai jaddada cewa ƙungiyoyin ƙasashe, kulob, lig-lig, ‘yan wasa da magoya baya bai kamata su zama ƙarƙashin muradun masu zuba jari ba.

UEFA ta kuma sanar da cewa dukkan mambobinta sun amince cewa babu wata ƙungiyar ƙasa ta Turai da za ta halarci kowace gasa ta FIFA muddin ana ci gaba da wannan shiri.

“Bayan tattaunawar da aka yi a yau, babu wata ƙungiyar ƙasa ta UEFA da za ta shiga kowace gasa ta FIFA muddin wannan shiri yana nan, sai dai idan an yi watsi da shi gaba ɗaya tare da ba da tabbacin doka cewa FIFA ba za ta sake buɗe tsarin mulkinta ko gasanninta ga mallakar masu zaman kansu ba,” in ji sanarwar.

UEFA ta kammala da cewa za ta yi adawa da shirin da cikakken ƙarfi, tana mai cewa “akwai abubuwan da suka fi ƙarfin a sayar da su,” tare da sake jaddada cewa “Gasar Cin Kofin Duniya ta FIFA mallakar kwallon kafa ce.”

Wannan rikici ya biyo bayan sanarwar da FIFA ta yi a farkon makon nan cewa tana shirin kafa wani sabon kamfani mai kula da haƙƙoƙin kasuwanci na Gasar Cin Kofin Duniya da sauran gasa, inda za ta bai wa masu zuba jari na waje damar mallakar ƙaramin kaso na hannun jari.

FIFA ta ce wannan shiri zai iya samar da fiye da dala biliyan 10 domin bunƙasa harkokin kwallon kafa cikin shekaru huɗu masu zuwa, tare da jaddada cewa za ta ci gaba da riƙe ikon tafiyar da harkokin mulki da yanke shawarar wasanni.

Sai dai shirin ya fuskanci suka daga wasu masu ruwa da tsaki a harkar kwallon kafa, ciki har da ƙungiyar European Leagues da ƙungiyar kare haƙƙin ‘yan wasa ta FIFPRO Europe, waɗanda ke nuna damuwa cewa shigar masu zuba jari masu zaman kansu zai iya raunana tsarin shugabanci da mutuncin kwallon kafa na dogon lokaci.

Post a Comment

Previous Post Next Post