An Cike Gurbin Kujerun Aikin Hajjin Kano Guda 3,050 na 2027

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da cewa an sayar da dukkan kujeru 3,050 da aka ware wa jihar domin gudanar da aikin Hajjin shekara ta 2027.

Babban Daraktan Hukumar, Abubakar Ibrahim Matawalle, ya ce an samu nasarar ne bayan kira ga maniyyata da ke buƙata da su aika masu sakonni su biya kuɗaɗen Hajji tare da kammala takardunsu.

Ya kuma ce akwai sama da mutum 200 da ke jiran samun gurbi idan wasu suka gaza cika sharuddan tafiya.

Matawalle ya gargaɗi waɗanda suka biya kuɗin hajji amma har yanzu ba su gabatar da fasfofinsu na intanet (e-passport) ba da su yi hakan kafin ranar 5 ga Satumba, yana mai cewa duk wanda ya gaza zai iya rasa kujerarsa duk da ya biya kuɗin hajjin.

Ya ce hukumar na shirin inganta ayyukan Hajjin 2027, ciki har da rage yawan gidajen da ake saukar da alhazai a Saudiyya domin sauƙaƙa kulawa da su da samar musu da abinci, kula da lafiya da sauran buƙatu.

Post a Comment

Previous Post Next Post