Masu kada ƙuri'a a Guinea-Bissau za su kada ƙuri'ar raba gardama a yau a kan ko za a amince da wani sabon kundin tsarin mulki da zai ƙara wa shugaban ƙasar iko.
Ƙuri'ar ta zo ne ƙasa da wata goma bayan sojoji sun ƙwace mulki a ƙasar da ke yammacin Afirka.An shirya gudanar da zaɓen gama gari a watan Disamba mai zuwa domin mayar da mulkin farar hula bayan juyin mulkin da aka yi a kasar.
Sai dai babbar jam'iyyar adawa ta ƙi shiga wannan ƙuri'ar raba gardaman.