Rahoton na Africom ya ce horon ya mayar da hankali kan sarrafa jirage marasa matuƙa, sarrafa makamai, cire bama-bamai, kula da waɗanda suka ji rauni da kuma dabarun yaƙi ga ƙaramar tawagar soji.
"Amurka da Najeriya na gudanar da aikin bayar da horo a sansanin horon soji da ke a Bauchi, Najeriya, bisa manufar musayar ƙwarewa, ƙarfafa abokan hulɗa da kuma yauƙaƙa alaƙa tsakanin ɓangarorin biyu," a cewar bayanin.
Horon na zuwa ne bayan a watan Yuli Amurka ta sanar da janye akasarin dakarunta da ta tura Najeriya domin wani aikin yaƙi da ta'addanci na musamman, yayin da ƙasashen biyu suka ci gaba da shirinsu na musayar bayanan sirri da tsaro.
A ƙarshen shekarar 2025 ne ƙasashen biyu suka ƙulla wata alaƙa ta tsaro bayan shugaban Amurka Donald Trump ya yi zargin cewa ana gallaza wa Kiristoci a Najeriya tare da matsa wa hukumomin Najeriyar lamba kan su magance matsalar tsaro.