Abbas Ya Nemi Kafa Diflomasiyyar Majalisa Tsakanin Najeriya da Kyuba

Kakakin Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Abbas Tajudeen, ya nemi a kafa tsarin diflomasiyyar majalisa domin ƙarfafa hulɗar Najeriya da Kyuba a fannoni da suka haɗa da kiwon lafiya, ilimi, bincike da kuma zuba jari na musamman.

Rt. Hon. Abbas Tajudeen

Abbas ya yi wannan kira ne a Abuja yayin da ya karɓi tawagar ƙasar Kyuba ƙarƙashin jagorancin Hon. Fernando González Llort, fitacce a ƙasar kuma shugaban Cibiyar Abokantaka ta Kyuba (ICAP). Kakakin, wanda Mataimakinsa, Hon. Benjamin Kalu, ya wakilta, ya bayyana cewa akwai buƙatar zurfafa dangantaka tsakanin ƙasashen biyu.

Ya lissafo muhimman fannoni da za a yi aiki a kai, ciki har da diflomasiyyar majalisa, kiwon lafiya, kasuwanci da al’adu, kimiyyar halittu da masana’antar magunguna.

Abbas ya ce hukumar Abokantakar Majalisar Najeriya da ta Kyuba za ta zama hanyar samar da yarjejeniyoyi, amincewar majalisa, da shirye-shiryen da za su haifar da sakamako kai tsaye. Ya ƙara da cewa akwai buƙatar a juya kusanci na al’adu da ake da shi a waƙa, wasanni da adabi zuwa damar kasuwanci ga ’yan Najeriya.

A ɓangaren kiwon lafiya, Kakakin ya yaba da rawar da Kyuba ta taka wajen tura likitoci zuwa ƙasashe daban-daban, yana mai cewa haɗin gwiwa a horaswa da samar da magunguna da rigakafi zai taimaka wajen ƙarfafa tsarin lafiya a Najeriya.

Shugaban tawagar Kyuba, Fernando González Llort, ya yaba da dangantakar da ke tsakanin ƙasashen biyu, yana mai cewa akwai buƙatar ƙarfafa musayar ziyara da haɗin kai tsakanin majalisun dokokin Najeriya da na Kyuba. Ya kuma bayyana sha’awar ƙasarsa na ƙara hulɗa da Najeriya a fannin tattalin arziƙi.

Llort ya miƙa gayyata ga Mataimakin Kakakin Majalisar Najeriya domin ziyartar Kyuba, inda za a ci gaba da tattaunawa kan diflomasiyyar majalisa da sauran fannoni na moriyar juna.

Abu-Ubaida Sani

I provide language services such as translation, transcription, proofreading, interpretation, etc in the Hausa language. I also outsource in Pidgin, Yoruba, Igbo, Fulah, and Kanuri. Contact me through email: abuubaidasani5@gmail.com or WhatsApp: +2348133529736

Post a Comment

Previous Post Next Post