Dangote Ya Zargi NUPENG Da Dora Kudin Lodin Manyan Motoci, Ya Ce Suna Haifar Da Tsadar Mai

Shahararren ɗan kasuwa kuma mafi arziki a Afirka, Aliko Dangote, ya zargi Ƙungiyar Ma’aikatan Dakon Mai da Gas na Najeriya (NUPENG) da ɗora kuɗaɗe har ₦50,000 a kan kowace babbar mota da ke ɗaukar man fetur daga sabuwar matatar man fetur ɗinsa.

Dangote

Dangote ya bayyana haka ne a yayin da yake mayar da martani kan ƙorafin NUPENG cewa kamfaninsa na hanawa direbobin motocin CNG guda 4,000 da ya ƙaddamar shiga ƙungiya.

“Ina gaya muku gaskiya: kowace mota da za ta ɗauki mai daga nan, NUPENG na karɓar kusan ₦48,000 zuwa ₦50,000. Idan kuma wasu masu ruwa da tsaki suka ƙara nasu, kuɗin zai kai ₦80,000 zuwa ₦84,000. To wa zai biya wannan kuɗi? A ƙarshe, jama’a ne za su sha wahala,” in ji shi.

Ya ce irin waɗannan kuɗaɗen “rent-seeking” ne - wato cin moriya ba tare da wani aiki ba - wanda ke rage inganci a harkar rarraba mai. Dangote ya kuma tuna yadda a da, lokacin da yake shigo da man fetur daga waje, masu sufuri suka shaƙe masa rai, abin da ya sa daga baya ya samar da motocin sufuri nasa ƙarƙashin kulawar ɗan’uwansa.

“Yanzu da muka fito da motocin CNG ɗinmu, ba za mu bari a sake riƙe mu da garkuwa ba. Idan babu jigilar mai, babu abin da za mu iya yi,” in ji shi.

Dangote ya jaddada cewa, ko da yake ya amince ma’aikata na da ’yancin shiga ƙungiya, bai kamata a tilasta wa kowa ba. “Ko addini ma zaɓi ne; ba za ka tilasta wa kowa ya sauya akida ba,” in ji shi.

Saɓanin haka, lokacin da aka nemi jin ta bakin Shugaban NUPENG, Comrade Williams Akporeha, bai tabbatar da zargin ba, bai kuma karyata shi gaba ɗaya ba. A maimakon haka ya mayar da martani cikin zolaya: “₦50,000 yanzu? Ashe ba ₦1 a kowace lita ba ne?”

Tun a baya dai, yayin da ake ta maganganu a kafafen sada zumunta cewa ƙungiyar na karɓar ₦1 a kowace lita, Akporeha ya ce: “Ba za ka hana mutane su faɗi ra’ayinsu ba. Amma duk wanda ya yi zargi, sai ya gabatar da hujja.”

Masana harkar man fetur sun nuna damuwa kan yadda ƙungiya za ta zama tamkar mai karɓar haraji, suna mai gargadin cewa hakan zai ƙara tsadar man fetur a tashoshi, alhali mutane ke ci gaba da fama da tsadar rayuwa a ƙasar.

Abu-Ubaida Sani

I provide language services such as translation, transcription, proofreading, interpretation, etc in the Hausa language. I also outsource in Pidgin, Yoruba, Igbo, Fulah, and Kanuri. Contact me through email: abuubaidasani5@gmail.com or WhatsApp: +2348133529736

Post a Comment

Previous Post Next Post