MDD Ta Tsawaita Takunkuman Da Aka Ƙaƙabawa Iran.
Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ta tabbatar da cewa takunkuman da ta ƙaƙabawa Iran sun ci gaba da aiki, duk da ƙoƙarin da hukumomin ƙasar suka yi na neman sassauci. Wannan mataki ya biyo bayan rashin cimma matsaya tsakanin ƙasashen duniya da Iran kan batun makamashin nukiliya.
Rahotanni sun nuna cewa takunkuman sun haɗa da taƙaita harkokin kasuwanci, safarar makamai, da kuma wasu muhimman hulɗoɗin tattalin arziki da sauran ƙasashen duniya.
Masana harkokin siyasa sun ce wannan tsawaita takunkumi zai ƙara matsawa Iran lamba a fagen diplomasiyya da kuma tattalin arzikinta.