Mutum 40 sun Mutu Bayan Hari Kan Makarantar Yanmatar Iran

Wani jami'i a Iran ya shaida wa kamfanin dillancin labaran ƙasar, IRNA cewa mutum 40 ne harin Ira'ila ya kashe a wata makarantar furamaren ƴanmata da ke garin Minab a lardin Hormozgan na kudancin ƙasar.

Gwamnan lardin, Mohammad Radmehr ya ce fiye da mutum 48 ne suka jikkata yayin da ake sa ran adadin waɗanda suka mutu zai ƙaru.

Kawo yanzu dai BBC ba ta ita tabbatar da sahihancin labarin ba - Ana hana manyan kafofin yaɗa labarai na duniya izinin shiga Iran, wani abu da ke taƙaita damarsu ta tattara labaran haƙiƙanin abin da ke faruwa a ƙasar.

Post a Comment

Previous Post Next Post