Kwamitin Tsaro na MDD ya kira Taron Gaggawa

Kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya kira taron gaggawa yau a birnin New York na Amurka.

Taron na zuwa ne bayan da Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniyar, Antonio Guterres ya yi Allah wadai da matakin soji a yankin Gabas ta Tsakiya.

Cikin wata sanarwa da ya fitar, Mista Gutterres ya ce ''matakin zai kawo cikas ga tsaro da zaman lafiyar duniya''.

Ya kuma yi kiran gaggauta kawo ƙarshen yaƙin.

Post a Comment

Previous Post Next Post