Taron na zuwa ne bayan da Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniyar, Antonio Guterres ya yi Allah wadai da matakin soji a yankin Gabas ta Tsakiya.
Cikin wata sanarwa da ya fitar, Mista Gutterres ya ce ''matakin zai kawo cikas ga tsaro da zaman lafiyar duniya''.
Ya kuma yi kiran gaggauta kawo ƙarshen yaƙin.