Firaministan Senegal Ya Soki Juyin Mulkin Guinea-Bissau

Firaministan Senegel Ousmane Sanko ya bayyana juyin mulkin da aka yi a Guiene-Bissau a matsayin abin da bai dace ba.

Mista Sanko ya buƙaci a ci gaba da bayar da damar tattara sakamakon zaɓe domin bayyana wanda ya yi nasara a zaɓen.

Yayin da yake jawabi ga majalisar dokokin ƙasar a birnin Dhakar, Mista Sanko ya ce dole hukumar zaɓen ƙasar ta bayyana wanda ya yi nasara a zaɓen.

Tun kafin bayyana zaɓen shugaban ƙasar Omaru Sissico-Embalo ya tsere daga ƙasar, inda ya ce sojoji sun ƙwace mulkin ƙasar.

Post a Comment

Previous Post Next Post