Yayan Sheikh Dahiru Bauchi Sun Yi Wa Jama’a Godiya

Yayin da ake ci gaba da alhinin rasuwar fitaccen malamin addinin musulucin nan na Najeriya, Sheikh Dahiru Bauchi, ƴaƴansa sun bayyana godiyarsu ga mutanen da suka halarci jana'izarsa.

Yayin wata hira da ƴarsa, Maryam Dahiru Bauchi ta shaida wa BBC cewa babu abin da za su ce game da rasuwar mahaifinta sai godiyar Allah.

''Alhamdulillahi mun rabu da mahifinmu lafiya, kuma muna fatan Allah ya sada shi da masoyinsa'', in ji Maryam wadda ta bayyana cikin sassanyar murya cike da alhini.

Maryam Dahiru Bauchi ta kuma gode wa ɗimbin al'ummar da suka halarci jana'izar mahaifin nata.

''Ba abin da za mu ce wa mutane sai godiya, da fatan Allah ya mayar da kowa gidansa lafiya'', in ji ta.

Dubun dubatar mutane ne daga ciki da wajen Najeriya ne suka halarci jana'izar fitaccen malamin addinin Musuluncin da ka gudanar a birnin Bauchi.

Post a Comment

Previous Post Next Post