Tinubu Ya Ba Da Umarnin Janye Yansanda Daga Gadin Manyan Mutane

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya bayar da umarnin janye dakarun 'yansanda daga gadin manyan mutane domin mayar da su aikin tsaro.

Tinubu ya bayar da umarnin ne yayin ganawar da ya yi da shugabannin tsaron ƙasar a yammacin yau Lahadi, ciki har da Sufeto Janar na "Yansanda s Kayode Egbetokun.

"Umarnin fadar shugaban ƙasa ya ce daga yanzu duk mutumin da ke son jami'an tsaro su yi gadinsa sai dai ya nemi jami'an tsaron Nigeria Security and Civil Defence Corps," a cewar wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa Bayo Onanuga ya fitar.

"Sassan Najeriya da dama, musamman a karkara, ba su da isassun 'yansanda, abin da ke ƙara ta'azzara aikin tsaron al'umma."

Post a Comment

Previous Post Next Post