TINUBU YA MIKA SUNAYEN SABBIN JAKADU 32 GA MAJALISA

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya mika sunayen mutane 32 da ya zaba a matsayin jakadu zuwa Majalisar Dattawa domin tantancewa da amincewa.

A cewar wata sanarwa da Mai Bawa Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Bayani da Tsara Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Asabar, jerin sunayen sun haɗa da jakadu 17 na siyasa da jakadu 15 na ƙwararru, waɗanda za a tura zuwa ƙasashe da kungiyoyin duniya masu muhimmanci ga harkokin diflomasiyyar Najeriya.

Sunayen da suka fito fili sun haɗa da:

  • Barrister Ogbonnaya Kalu (Abia)

  • Reno Omokri (Delta) – Tsohon hadimin tsohon Shugaba Goodluck Jonathan

  • Farfesa Mahmood Yakubu (Bauchi) – Tsohon Shugaban INEC

  • Erelu Bisi Angela Adebayo (Ekiti) – Tsohuwar Matar Gwamnan Ekiti

  • Ifeanyi Ugwuanyi (Enugu) – Tsohon Gwamnan Jihar Enugu

  • Tasiu Musa Maigari (Katsina) – Tsohon Kakakin Majalisar Dokokin Katsina

  • Yakubu N. Gambo (Plateau) – Tsohon Kwamishina, kuma tsohon Mataimakin Sakataren Hukumar UBEC

  • Farfesa Nora Ladi Daduut (Plateau) – Tsohuwar Sanata

  • Otunba Femi Pedro (Lagos) – Tsohon Mataimakin Gwamna

  • Chief Femi Fani-Kayode (Osun) – Tsohon Ministan Sufuri

  • Barr. Nkechi Linda Ufochukwu (Anambra) – Lauya

  • Fatima Florence Ajimobi (Oyo) – Tsohuwar Matar Gwamnan Oyo

  • Lola Akande (Lagos) – Tsohuwar Kwamishina

  • Grace Bent (Adamawa) – Tsohuwar Sanata

  • Dr. Victor Okezie Ikpeazu (Abia) – Tsohon Gwamnan Abia

  • Sanata Jimoh Ibrahim (Ondo) – Dan kasuwa, tsohon Sanata

  • Ambassador Paul Oga Adikwu (Benue) – Tsohon Jakadan Vatican

  • Enebechi Monica Okwuchukwu (Abia)

  • Yakubu Nyaku Danladi (Taraba)

  • Miamuna Ibrahim Besto (Adamawa)

  • Musa Musa Abubakar (Kebbi)

  • Syndoph Paebi Endoni (Bayelsa)

  • Chima Geoffrey Lioma David (Ebonyi)

  • Mopelola Adeola-Ibrahim (Ogun)

  • Abimbola Samuel Reuben (Ondo)

  • Yvonne Ehinosen Odumah (Edo)

  • Hamza Mohammed Salau (Niger)

Jakadu masu ƙwarewa sun haɗa da:
Ambassador Shehu Barde (Katsina), Ambassador Ahmed Mohammed Monguno (Borno), Ambassador Muhammad Saidu Dahiru (Kaduna), Ambassador Olatunji Ahmed Sulu Gambari (Kwara), Ambassador Wahab Adekola Akande (Osun).

Ana sa ran za a tura su zuwa muhimman ƙasashe irin su China, India, South Korea, Canada, Mexico, UAE, Qatar, South Africa, da Kenya, tare da wuraren aikace-aikace na din-din-din kamar Majalisar Ɗinkin Duniya (UN), UNESCO da Tarayyar Afirka (AU).

Za a bayyana wuraren da za su tafi aiki ne bayan Majalisar Dattawa ta tantance su ta kuma amince da nadin nasu.

Post a Comment

Previous Post Next Post