Jakadan MDD Ya Gana Da Shugaban Sudan Don Tattauna Tsaro Da Halin Jin Kai A Kasar

Jakadan Majalisar Dinkin Duniya, Ramtane Lamamra, ya gana da shugaban Sudan kuma shugaban sojoji, Lt Janar Abdel Fattah al-Burhan, a birnin Port Sudan domin tattauna hanyoyin shawo kan mummunar yaƙin basasar da ya dabaibaye kasar, musamman a ɓangaren tsaro da agajin jin kai.

MDD
A wata sanarwa da majalisar mulkin kasar ta fitar, Burhan ya bayyana cewa gwamnatin Sudan na neman zaman lafiya ta yadda zai dace da muradun al’ummar ƙasar.

Ya kuma jaddada buƙatar samun haɗin gwiwa da Majalisar Dinkin Duniya domin inganta tsaro da zaman lafiyar kasar tare da cimma muradun aikin jin kai.

Shugaban sojojin ya kuma maimaita cewa wannan yaki zai kare ne kawai idan dakarun soja sun samu nasara gaba daya, tare da janyewar dakarun RSF daga yankunan da take riƙe da su a halin yanzu.

Post a Comment

Previous Post Next Post