Yan Bindiga Sun kashe Mutum 6 a Jihar Neja - Yansanda

Ƴan sanda sun ce mutane 6 ne suka mutu ranar Juma'a a wani sabon hari da aka kai kusa da ƙauyen Wawa da ke jihar Neja da ke yankin a arewa ta tsakiyar Najeriya.

A cewar rundunar ƴan sandan, ƴan bindigar sun yi wa wani uba da ɗansa kwanton ɓauna a lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa ziyarar ma’aikatan gona a wani ƙauye mai suna Damala.

Ɗan yayi nasarar tserewa inda ya nemi agaji. Ƴan uwa da ƴa sa-kai da suka je neman mahaifin yaron su ma ƴan fashin sun kai musu hari.

Daga bisani jami’an tsaro sun gano gawarwaki shida. Mutumin da aka fara kai wa hari da kuma wani mutum ɗaya kuma sun yi ɓatan dabo.

An kai waɗanda lamarin ya shafa babban asibitin garin Wawa. Jami’ai sun ce ana gudanar da bincike, amma lamarin ya ƙara zurfafa fargabar da ake yi kan tabarbarewar tsaro a yankunan da ke kewaye da hanyar Neja zuwa Kwara.

Garin Wawa dai yana kusa da gandun dajin Kainji kuma ya haɗa jihohin Neja da Kwara, da Jamhuriyar Benin, wanda ke bai wa ƴan bindiga damar kai hare-hare kan sansanonin sojoji su kuma ƙetara zuwa wasu ƙasashe.

Post a Comment

Previous Post Next Post