Hatsarin Jirgin Kasa ya Kashe Mutum Daya a Italiya

Aƙalla mutum ɗaya ne ya mutu, wasu 39 kuma aka ce sun samu munanan raunuka, bayan da wani jirgin ƙasa mai amfani da lantari ya kauce hanya a birnin Milan na arewacin Italiya.

Jirgin mai cike da cunkoson jama'a yana tafiya ne a kan titin Vittorio Veneto na Milan a lokacin da ya ci karo da gefen wani gini.

Ana tunanin jirgin ya kaɗe mutumin da ya mutu ne , kuma yawancin waɗanda suka jikkata fasinjoji ne.

Motocin ɗaukar marasa lafiya da dama suna wurin kuma akwai rahotannin mutane da suka maƙale a cikin tarkacen jirgin.

Fasinjoji sun bayyana jin wani ƙara a ƙarƙashin jirgin, jim kaɗan kafin jirgin ya faɗi.

Post a Comment

Previous Post Next Post