Mahara sun Turo Wasiƙa Kafin Kai Hari a Kwara'

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin tura bataliyar soji zuwa sassan jihar Kwara, bayan mummunan harin da ya yi sanadiyyar kisan gomman mutane a ƙaramar hukumar Kaiama ta jihar. 

Shugaba Tinubu a wata sanarwa da kakakinsa Bayo Onanuga ya fitar ranar Laraba da dare ya kuma naɗa kwamandan da zai jagoranci rundunar sojin da za a tura jihar Kwara, wadda za ta gudanar da aikin wanzar da zaman lafiya da aka yi wa laƙabi da 'Operation Savanna Shield'.

Gwamnatin Najeriya ta ɗauki wannan mataki ne bayan harin da aka kai wa ƙauyen Woro, inda rahotanni ke cewa an tattara gawarwakin mutane 78 da maharan suka kashe.

Hon Sa'idu Baba Ahmed, ɗan majalisar dokokin jihar Kwara ne, kuma ya shaidawa BBC cewa sun yi jana'izar sama da mutane 70 daga cikin waɗanda maharan suka kashe.

Ya ce ''abin da dai na gani, waɗanda muka yi wa sallah, mutum 78 ne amma akwai waɗanda aka ƙone a cikin gidajensu, ba mu san adadin su ba tukun. An hallaka mutum zai kai 170.''

Hon. Baba Ahmed ya kuma ce maharan ''sun wuce da mata 38,'' daga ƙauyukan da suka kai wa hari.

Ya yi bayanin cewa sarkin garin ya shaida masu cewa maƙonni uku da suka wuce an rubuta mashi wasiƙa cewa za su zo su yi wa'azi a wajen, lamarin da ya sa shi kuma sarkin ya bayar da rahoto ga jami'an tsaro.

Ɗan majalisar ya ce daga cikin mutanen da suka yi wa jana'iza a ranar Laraba da yamma, akwai maza 75 da mata uku, sannan akwai wasu mutum bakwai da aka garzaya da su asibiti saboda munanan raunin da suka samu.

Post a Comment

Previous Post Next Post