Tinubu zai kai Ziyarar Aiki a Birtaniya

Fadar Buckingham ta ce a karon farko cikin shekara 37, shugaban Najeriya zai kai ziyara aiki Birtaniya, inda sarki Charles III da sarauniya Camilla za su karɓi baƙoncin shugaban Bola Tinubu.

Shugaba Tinubu da maiɗakinsa Oluremi Tinubu sun amince su ziyarci Sarki Charles a fadarsa daga ranar 18 zuwa 19 ga watan Maris.

Ziyarar aiki da shugaban Ƙasa ke kaiwa fadar Buckingham ta kasance wata muhimmiyar hanyar inganta alaƙar diflomasiyya tsakanin ƙasashe da Birtaniya, inda ake tattauna hanyoyin cin gajiyar juna.

Rabon da shugaban Najeriya ya kai irin wannan ziyara Birtaniya tun a 1989, lokacin da Janar Ibrahim Babangida ya ziyarci mariganya Sarauniya Elizabeth II, inda ya shafe kwanaki huɗu.

Post a Comment

Previous Post Next Post