Iran ta kama Mutum 30 Bisa Zarginsu da yi wa Amurka da Isra'ila leken Asiri

Kafar yaɗa labaran Iran ta ruwaito cewa hukumomin ƙasar sun kama mutum 30 bisa zarginsu da yi wa Amurka da Isra'ila leƙen asiri.

Kafar ta ce daga cikinsu akwai mutum ɗaya ɗan ƙasar waje, kuma ma'aikatar tattara bayanan sirrin ƙasar ne suke tsare da su.

Haka kuma an kama wasu waɗanda Iran ta bayyana "masu leƙen asiri na cikin gida" da "wakilan Isra'ila da Amurka" a kwanakin baya.

Post a Comment

Previous Post Next Post