Jakadan Najeriya a Amurka, Ambasada Kayode Are, ya bayyana cewa da yiwuwar Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai kai ziyarar aiki a birnin Washington kafin ƙarshen wa'adinsa, ya na mai cewa hulɗar diflomasiyya da ke ci gaba tsakanin Najeriya da Amurka ta samar da kyakkyawan tushe domin yiwuwar ganawa tsakanin Tinubu da Shugaban Amurka, Donald Trump.
Are ya bayyana hakan ne a shirin Inside Sources with Laolu Akande na tashar Channels Television.
Ya ce duk da cewa shirye-shiryen tafiye-tafiyen shugabanni na dogara da muhimman la'akari na diflomasiyya, dangantakar da ke tsakanin Shugaba Tinubu da Shugaba Trump tana da kyau, kuma ana ci gaba da tattaunawa tsakanin ƙasashen biyu a matakai daban-daban.
Jakadan ya ce ziyarar shugaba Tinubu a hukumance zuwa Amurka za ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwar dabarun ƙasashen biyu, ta bunƙasa alaƙar siyasa da tattalin arziki, tare da samar da sabbin damar kasuwanci, zuba jari da haɗin gwiwa a fannin tsaro.
Are ya ce dawo da ƙwarin hulɗar diflomasiyya da farfaɗo da ayyukan ofishin jakadancin na buƙatar lokaci, yana mai jaddada cewa jakadu na taka muhimmiyar rawa wajen ƙarfafa hulɗar siyasa, jawo masu zuba jari, bunƙasa kasuwanci da kare muradun ƙasarsu a ƙasar da suke wakilta.
Ya ce manufofin shige da fice na Amurka a halin yanzu sun shafi 'yan Najeriya masu neman tafiya don yawon buɗe ido, kasuwanci, karatu da ziyartar iyalai, yana mai ƙarawa da cewa ofishin jakadancin na karɓar tambayoyi kan batutuwan biza kusan a kullum.
A ƙarshe, jakadan ya buƙaci 'yan Najeriya masu tafiya Amurka da su mutunta dukkan sharuɗɗan bizar da aka ba su, yana mai gargadin cewa karya dokokin shige da fice ko wuce wa'adin biza na iya cutar da mutum tare da bata sunan Najeriya.
