Amina bt. Wahb (AS) (Da Larabci: آمنة بنت وَهْب ) (shekara arba'in da shida kafin Hijira / 575-6), mahaifiyar Manzon Allah (SAW) ce, kuma daya daga cikin matan Kuraishawa masu daraja. Amina ta auri Abdullahi ibn Abdul al-Muttalib (AS) a shekaru hamsin da hudu ko hamsin da uku kafin Hijira (568 zuwa 570). Duk da karancin lokacin zamantakewar aurensu ta haifi Muhammad (SAW), a shekaru hamsin da biyu kafin Hijira (570). Lokacin Annabi Muhammad (SAW) yana da shekaru hudu ko shida, Amina ta rasu a wani yanki da ake kira al-Abwa' yayin da ta dawo daga Madina.
Haihuwa da Zuri'a
An haifi Amina a Makka. Mahaifinta, Wahb, babban dan kabilar Banu Zuhra ne. Ana kiran su "Manafayn" saboda girmamawa. Mahaifiyar mahaifinta, Atika, al-Awqas b. Murra b. 'Yar Hilal Sulamiyya, tana daya daga cikin Atika ukun da Manzon Allah (SAW) yake alfahari da kasancewarsa zuriyarta, ya ce: "Ni ne zuriyar Awatik daga Banu Sulaym. Mahaifiyarta ita ce Barra bt. Awf.
Hakika mahaifar Amina bint Wahb ita ce mafi daukaka da daraja a cikin dukkan mahaifa, domin ita ce mahaifar da ke dauke da hatimin dukkan Annabawa kuma shugaban manzanni.
A cikin wannan mahaifa ne mai girma tayin (Manzon Allah) ya zauna.
Ita wannan zuriya ta kasance daga cikin zuriyar mutane tun daga zamani zuwa zamanai har sai da Allah cikin hikimarSa ya hukunta ta cikin Abdullahi bn Abdul Muddalib, (AS) matashin Kuraishawa wanda ya yi fice a zamaninsa.
Abdullahi bn Abdul Muddalib ya samu fansa daga yanka, bayan mahaifinsa ya yi alkawarin yanka shi kuma ya nemi ya cika alkawarinsa. Shi ne mutum mafi daraja da Larabawa suka sani.
Ba a yanka shi ba da iznin Allah, domin zaɓin Ubangiji ya tabbata kuma ya kafu a cikin tarihin ɗan adam, dukansu suna shaida da cikakken iznin Allah.
“Allah Ya zabi Adam da Nuhu (Nuhu) da Iyalan Ibraheem (AS) da Iyalan Imrana a kan ’yan Adam (Mutane da Aljanu) zuriya da sashe, kuma Allah Shi ne Mai ji, Mai gani kuma Masani." (Alkurani 3:33-34).
Abdullahi ya fita tare da mahaifinsa Abdul-Muttalib bayan ya tsira daga hadaya. Sai wata mata daga Bani Asad bn Abdul Uzza ta gan shi a gefen Ka'aba, sai ta ce masa, bayan ta kalli fuskarsa,
zan ba ka kwatankwacin rakuman da aka yanka domin fansarka idan zaka yi tarayya da ni yanzu.
Domin ta ga wani abu na musamman a jikinsa. Abdullahi (AS) ya karba mata da cewa gara ya mutu da ya aikata haram kuma mai daraja ya kiyaye mutuncinsa da addininsa hakan ya fi cancanta.
Abdulmuttalib ya zaɓi Amina bint Wahb daga kabilar zuhur ta zama matar dansa Abdullahi. A lokacin Amina ta kasance mafi kyawun macen Kuraishawa a tsatso da matsayi.
Wata ‘yar duba daga Tibala wacce aka fi sani da Fatimah bint Murr al-Khath’amiyah ita ma ta ga Abdullahi. Wannan mata ta kasance daya daga cikin mafi kyawu da tsaftar matan larabawa. Sai ta ga hasken annabci a fuskar Abdullahi, sai ta mika masa bukatar aurenta amma ya ki yarda da ita.
Labarin wani Annabi da zai zo daga ‘ya’yan Isma’il (amincin Allah ya tabbata a gare shi) yana yaduwa a tsakanin Larabawa a ko’ina a cikin yankin.
Wannan labari ya dogara ne akan abin da ma'abuta littafi suka ba da labari da abin da suke ba da labari daga abin da aka rubuta a cikin Attaura, a fakaice da bayyane. Har ila yau, mutane sun gano hakan daga masu duba da masu ilmin taurari.
Duk da Abdullahi bn Abdul Muddalib (AS) matashi ne kyakkyawa, ya mallaki tarbiyya mai ban mamaki da daukaka saboda cewa yana da tsafta da kyawawan dabi'u yan mata da yawa sun nemi aurensa, amma Allah ya kaddara cewa Amina za ta kasance Matar Abdullah.
Amina ta haihu Annabi mai daraja. Bayan 'yan watanni da daukar ciki, Abdullahi ya yi tafiya zuwa kasar Sham (Syriya bisa ga ma'anar yanayin kasa na Larabawa yanki ne da ya kunshi Palastinu, Jordan, Siriya da Lebanon da Birnin Gaza da ke gabar tekun Palastinu). Daya daga cikin manyan garuruwan da ‘yan kasuwar Kuraishawa suke yawan zuwa). Amma a kan hanyarsa ta dawowa sai ya kamu da rashin lafiya, ya zauna a wurin kawunsa na uwayensa daga kabilar Bani Najjaar a Yasriba, inda suka rinka kula da shi. A inda ya rasu ne saboda rashin lafiyar da ya yi fama da ita.
Amina ta ji takaicin rasuwar mijin da take so, wanda ya zauna da ita watanni kadan bayan aurensu. Tayi kuka sosai, ta zama maitakaba tun ba ta haihu ba. Amma ta hakura ta daure. Ta sami kulawa sosai daga Abdul-Muddalib. Wasu rahotannin tarihi sun nuna cewa, Abdullahi ya rasu jim kadan bayan haihuwar Manzon Allah (SAW).
Haihuwar Muhammad (SAW).
Ta haife shi ne a ranar 12 ga watan Rabiu'auwal, 570. Labarin haihuwarsa ya ba Banu Hashim farin ciki sosai har Abu Lahab ya 'yanta kuyangarsa Thuwayba al-Aslamiyya wacce ta kawo labarin haihuwar. Abdul al-Muttalib ya sa masa suna Muhammad. Da Kuraishawa ta tambayi dalilin sunan jikansa, sai ya ce: “Ina son a yabe shi sama da kasa.
Tafiya zuwa Madina da Mutuwa
Amina ta dauki Muhammad don ta ziyarci kabarin mijinta Abdullah a madina a shekara ta bakwai ta giwaye. Kawun mahaifin Annabi Muhammad (SAW) daga Banu Najjar ne. Ta yi rashin lafiya lokacin da ta dawo daga Madina ta rasu a al-Abwa' Ummu Ayman ta dawo da Annabi Muhammad (SAW) zuwa Makka bayan kwana biyar.
