Djibouti Ta Nemi Tallafin Gaggawa Yayin da Dubban ’Yan Yemen Ke Tserewa Zuwa Kasar


Djibouti ta nemi taimakon ƙasa da ƙasa domin tunkarar ƙarin yawan ’yan Yemen da ke tserewa zuwa ƙasar, tana mai gargadin cewa adadin mutanen da ke shigowa ya riga ya zarce ƙarfin da ƙasar za ta iya ɗauka.

A cewar Ministan Harkokin Cikin Gida na Djibouti, Omar Abdi Said, sama da ’yan Yemen 2,500 ne suka isa ƙasar tun ranar Alhamis na makon da ya gabata.

Said ya bayyana a ranar Laraba cewa, “Muna sa ran adadin mutanen da suka rasa matsugunansu zai ƙaru zuwa kusan 10,000 a cikin makonni masu zuwa.”

Ya ƙara da cewa, “Yawan mutanen da ke shigowa ya riga ya zarce ƙarfin ƙasarmu, kuma matsin lamba na ƙaruwa yayin da tallafin kuɗi daga ƙasashen duniya ke raguwa. Muna kira ga Majalisar Ɗinkin Duniya da abokan hulɗarmu na ƙasa da ƙasa da su tattara tare da samar da tallafin kuɗi na gaggawa da ya dace da girman wannan matsala.”

A halin yanzu, ana gwabza kazamin faɗa a yammacin Yemen tsakanin mayakan Houthi da ke samun goyon bayan Iran da gwamnatin Yemen da ƙasashen duniya suka amince da ita, wadda Saudiyya ke marawa baya. Dubban ’yan Yemen ne suka nemi mafaka a Djibouti, wadda ke kallon Yemen kai tsaye ta ɗaya ɓangaren Bahar Maliya.

Ƙazantar rikicin na ƙara tsananta mummunan yanayin jinƙai a Yemen, wadda ke cikin ƙasashen da suka fi fama da talauci a Gabas ta Tsakiya.

Fiye da mutane miliyan 4.5 ne suka rasa matsugunansu tun bayan da ƙawancen da Saudiyya ke jagoranta ya shiga yakin basasar Yemen a shekarar 2015. Ƙaruwar tashin hankalin da ake gani a yanzu ta haifar da fargabar cewa mutane da dama za su sake rasa matsugunansu a cikin Yemen, tare da yiwuwar ƙarin ’yan kasar su tsere zuwa ƙasashen waje.

Ofishin Ƙungiyar Ƙasa da Ƙasa ta Kula da Hijira (IOM) da ke Djibouti ya bayyana a wani bidiyo da aka wallafa a shafin X ranar Laraba cewa ma’aikatansa da hukumomin ƙasar suna wuraren da ’yan Yemen ke isa, inda suke samar musu da abinci da ruwa.

Mai kula da ayyukan IOM a Djibouti, Safiya Ibrahim, ta yi gargadin cewa mutane da dama, ciki har da mata, yara, jarirai da marasa lafiya, na isa ƙasar a kullum.

Ta ce IOM na “dogaro da ƙarin tallafin kuɗi” domin ci gaba da gudanar da ayyukanta na agaji.

Djibouti ita ce ƙasa ta uku mafi ƙanƙanta a nahiyar Afirka, inda yawan al’ummarta bai kai mutum miliyan 1.2 ba.

Post a Comment

Previous Post Next Post