El-Sisi Na Masar Ya Yi Watsi Shirin Korar Falasdinawa Daga Gaza

 Shugaban Masar, Abdel Fattah el-Sisi, ya sake bayyana cewa Masar na ƙin duk wani shiri na korar ko raba Falasɗinawa da Gaza. Ya bayyana hakan ne a ranar Laraba, 16 ga Satumba, yayin ganawarsa da Shugaban Falasɗinawa Mahmoud Abbas a birnin Alkahira.

Abdel Fattah el-Sisi

El-Sisi ya jaddada cewa Masar ba za ta amince da duk wani yunƙuri na kawar da batun Falasɗinu ba. Ya kuma ce Masar za ta ci gaba da aiki tare da masu shiga tsakani domin aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wutar Gaza, da dakatar da ƙarin tashin hankali, da kuma tabbatar da shigar da tallafin jin ƙai zuwa Gaza. 

Wannan furucin ya zo ne bayan kalaman Ministan Tsaron Isra’ila Israel Katz, wanda ya ce sojojin Isra’ila za su ci gaba da yaƙin Gaza tare da aiwatar da wani shiri da ya shafi ƙaura ko ficewar Falasɗinawa daga yankin. 

Abbas ya yaba da matsayin Masar, yana mai jaddada cewa Gaza wani ɓangare ne na ƙasar Falasɗinu. El-Sisi ya kuma sake bayyana goyon bayan Masar ga kafa ƙasar Falasɗinu mai cin gashin kanta bisa iyakokin kafin Yunin 1967, tare da Gabashin Kudus a matsayin babban birninta.

Post a Comment

Previous Post Next Post