Muhawarar da ke gudana game da hauhawar farashin man fetur a Nijeriya wanda yanzu ya kai N1,500 a kowace lita ya haifar da ce-ce-ku-ce, inda masanin tattalin arziƙi da zamantakewa Abu-Ubaida Sani ya yi gargaɗi game da kuskuren kwatanta wannan farashi da na ƙasashen da suka ci gaba kamar Amurka da Birtaniya.
A cikin wani bayani mai ƙarfi game da halin da mazauna ƙasar ke ciki, Sani ya bayyana cewa kwatanta farashin fetur a Nijeriya da na ƙasashen da suka ci gaba rashin fahimtar matsalolin gaskiya ne, inda ya buƙaci masu tsara manufofi da 'yan ƙasa da su duba yanayin tattalin arziƙi gabaɗaya maimakon duba alƙaluma a ware.
A cewar Sani, kwatanta farashin fetur ba tare da la'akari da samun kuɗin shiga na mutane da ayyukan agaji, da tallafin gwamnati ba yaudarar kai ne. Abin tambayar shi ne: 'Mene ne matsakaitan 'yan ƙasa ke samu, mene ne gwamnati ke bayarwa, kuma me ke ragewa a aljihun ɗan ƙasa bayan biyan buƙatun yau da kullum?'
Sani ya jaddada cewa hauhawar farashin man fetur a Nijeriya yana bazuwa zuwa kowane fanni na rayuwa:
• Fetur yana shafar kuɗin sufuri.
• Sufuri yana shafar farashin abinci.
• Farashin abinci yana shafar kasafin kuɗin iyali.
• Kasafin kuɗin iyali yana shafar kusan komai na rayuwa.
Sani ya rufe da cewa idan ana son 'yan Nijeriya su biya farashin mai na ƙasashen da suka ci gaba, ya kamata su ma su samu kyakkyawan tsarin mulki da ayyukan agaji, da tsarin rage raɗaɗin rayuwa masu tafiya kafaɗa da kafaɗa.