Mataimakin Shugaban Kasar Nigeria Kashim Shettima Ya Gana da Shugaban Majalisar Dinkin Duniya Gutteres

 Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima, ya gana da sakatare janar na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD), António Guterres, a zauren majalisar da ke birnin New York, inda batun neman kujerar dindindin a kwamitin tsaro ya kasance kan gaba a tattaunawar.

Ganawar ta gudana ne bayan taron babban zauren Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 80 (UNGA80), inda Shettima ya gabatar da jawabin ƙasa a madadin Shugaba Bola Tinubu. Shettima ya jaddada bukatar MDD ta ƙara tallafa wa Najeriya don cimma burinta, musamman yadda ƙasar ke sha’awar samun kujerar dindindin a kwamitin tsaro.

BATUTUWAN DA AKA TATTAUNA 

Ministan harkokin waje, Yusuf Tuggar, ya shaida wa manema labarai cewa an tattauna kan ci gaban da ake son samu wajen aiwatar da muradun ci gaba masu ɗorewa (SDGs), batun sauyin yanayi da kuma haɗin kai don ƙarfafa dimokuraɗiyya a Najeriya da yankin Afirka. Haka kuma, Guterres ɗin ya yaba da rawar da Shettima ya taka wajen jaddada buƙatar Najeriya ta kujerar dindindin, tare da bayyana irin muhimmancin MDD a Najeriya, kasancewar dama ofisoshi da hukumomin majalisar da dama suna aiki a ƙasar.

BATUN FASAHAR ZAMANI DA WALWALAR JAMA'A

Ministan sadarwa da ƙirƙire-ƙirƙire, Bosun Tijani, ya bayyana cewa Guterres ya nuna farin ciki da nasarar Najeriya wajen ƙaddamar da samfurin fasahar AI mai harsuna da dama (multilingual AI model) na farko a nahiyar Afirka, wanda gwamnati ta tallafa. A cewarsa, Guterres ya buƙaci Najeriya ta taimaka wa sauran ƙasashen Afirka don kada a bar nahiyar baya a fannin na’urorin fasahar (AI).

A nasa ɓangaren, Ministan walwala, jin ƙai da rage talauci, Yusuf Sununu, ya ce Shettima ya bayyana ƙoƙarin gwamnatin Tinubu wajen rage talauci da tallafa wa jama’a. Ya ce gwamnati na da jadawalin al’umma da ta ƙunshi gidaje miliyan 18.9, inda aka riga aka tallafa wa sama da mutane miliyan 8.1 ta hanyar shirin bayar da kuɗin tallafi.

Sununu ya ce an kuma bayyana damuwa kan raguwar tallafin kuɗi daga wasu ƙungiyoyin MDD, ciki har da shirin WFP wanda ya tallafa wa sama da mutane miliyan 1.3 da kayan abinci.

TABBACIN GOYON BAYAN MDD

Sakataren-janar na MDD ya tabbatar wa Najeriya cewa za ta ci gaba da samun goyon baya wajen ƙara ƙarfin ma’aikatun gwamnati, tabbatar da sahihancin bayanan al’umma, da kuma samun karin tallafi don rage talauci da inganta jin dadin jama’a.

Kashim Shettima da Gutteres

A cewarsa, Guterres ya gode wa Shugaba Bola Tinubu da gwamnatin Najeriya baki ɗaya kan irin haɗin kai da suke bai wa MDD.

Post a Comment

Previous Post Next Post