An Yi Barazanar Hallaka Laftanar Ahmed Yerima

Da yammacin ranar Lahadi ne rahotonin yunƙurin kashe Laftanar Ahmed Yerima - matashin sojan da ya yi sa-in-sa da ministan Abuja, Nyesom Wike a makon da ya gabata - suka cika shafukan sada zumunta.

Rahotonnin sun yi iƙirarin cewa wasu matasa ne da ba a san ko su wane ne ba suka yi yunƙurin halaka sojan ruwan a Abuja, babban birnin ƙasar.

Laftanar AM Yerima ya ɗauki hankalin ƴan Najeriya a makon da ya gabata bayan da ya jagoranci tawagar wasu sojoji da suka hana ministan Abuja, shiga wani fili da ya yi zargin ana gina shi ba bisa ƙa'ida ba.

Ministan ya yi zargin cewa ana gina filin ne - wanda ake zargin mallakin tsohon babban hafsan sojin ruwan ƙasar ne - ba bisa ƙa'ida.

Lamarin da ya sa ya yi yunƙurin zuwa da kansa domin hanawa, to amma sai sojan - wanda aka ce an tura su ne domin gadin filin - ya dakatar da shi daga shiga wurin.

Rundunar ƴansandan birnin Abuja, mai alhakin kare samar da tsaro a birnin, ta musanta wannan iƙirari, tana mai cewa iƙirari ba shi da tushe balle makama.

Cikin wata sanarwa da rundunar ƴansandan Najeriya, reshen birnin na Abuja ta fitar ta hannun kakakinta, SP Josephine Adeh, ta ce babu inda aka samu irin wannan iƙirari.

''Rundunar ƴansanda reshen Abuja ta lura da abubuwan da ke yawo a shafukan sada zumunta, da ke zargin an yi yunƙurin kashe Lt. Ahmed Yerima.

Post a Comment

Previous Post Next Post