Tabbas Ana Kashe Kiristoci A Nijeriya, Nicki Minaj Ta Jaddada Wa Majalisar Dinkin Duniya

Shahararriyar mawaƙiyar gambara ta  Amurka Nicki Minaj ta goyi bayan Donald Trump, inda ta bayyana wa majalisar Dinkin Duniya cewa ba karya ba ne, ana kashe Kiristoci a Nijeriya.

Nicki Minaj

Shahararriyar mawakiyar Rap ta Amurka Nicki Minaj ta bi sawun shugaba Donald Trump, inda ta jaddada zargin da ya yi na cewa ana yi wa Kiristoci kisan kare dangi a Najeriya duk da ci gaba da musu da fadar mulki ta Abuja ke yi.

A yayin wata zantawa da aka shirya a jiya Talata a birnin New York bisa jagorancin jakadan Amurka a MDD Mike Waltz, fitacciyar mawakiyar mai shekaru 42 a duniya ta gode wa Shugaba Trump kan yadda ya dauki wannan batu da matukar muhimmaci.

Post a Comment

Previous Post Next Post