Tinubu Ya Bada Umurnin Yi Wa Dajin Neja Da Kwara Kawanya

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bai wa jami'an tsaro umurnin su yi wa dajin jihar Kwara ƙawanya, sakamakon ƙaruwar ayyukan ƴan bindiga a yankin.

Shugaban ƙasar ya kuma umurci sojojin sama su faɗaɗa ayyukansu na sa ido har zuwa tsakiyar dazukan inda ake tunanin ƴan ta'addan na ɓoya.

A cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban shawara kan sadarwa, Sunday Dare ya fitar, ya kuma ce shugaban ya bayar da umurnin yin hakan a yankunan Kebbi da Neja, inda ake sa ran ceto yara a Neja.

Ya kuma ce wajibi ne sojojin sama su riƙa aikin sa ido awa 24 domin taimaka wa aikin da sojojin ƙasa ke yi.

Post a Comment

Previous Post Next Post