Yanbindiga Sun Saki Mataimakin Shugaban Majalisar Jihar Kebbi

Rahotanni daga jihar Kebbi na cewa an sako mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar Kebbi dan ƴanbindiga suka yi garkuwa da shi kwanan baya.

Wata majiya daga majalisar ta shaida wa BBC cewa Muhammad Samaila Bagudo ya dawo cikin ƙoshi lafiya bayan kwanaki a hannun masu garkuwa.

Har zuwa lokacin haɗa wannan labarin dai babu cikakken bayani game da ko an biya kuɗin fansa kafin a sako shi, amma dai majiyar ta ce majalisar ta yi godiya ga dukkan waɗanda suka yi aiki tare don ganin ya kuɓuta daga hannun masu garkuwa da shi.

A ranar 31 ga watan Oktoba ne aka sace shi daura da gidansa da ke garin Bagudo.


Post a Comment

Previous Post Next Post