PDP Ta Kafa Kwamatocin Riƙo A Jihohin Enugu, Delta, Rivers

Babbar jam'iyyar adawa ta PDP a Najeriya ta ce ta kafa kwamatoci na riƙon ƙwarya da za su kula da shugaancin jam'iyyar a jihohin Enugu da Delta da Rivers - dukkansu a kudancin ƙasar.

Wata sanarwa da ta fitar a yammacin yau Juma'a, PDP ta ce kwamatin gudanarwa ne ya amince da kwamatocin riƙon bisa tanadin sashe na 29(2)(b) na tsarin mulkin jam'iyyar na 2025 da aka yi wa kwaskarima.

Zaɓukan shugabanci a jihohin kudu maso kudu na cikin abubuwan da suka ƙara jawo ruɗani a cikin jam'iyar, inda ɓangaren Ministan Abuja Nyesom Wike ke zargin an yi wa waɗanda suke goya wa baya ƙarfa-ƙarfa bayan sun cei zaɓen ta hanyar soke shi.

"Kwamatocin za su ɗauki ragamar shugabancin jam'iyyar a jihohinsu na tsawon abin da bai wuce kwana 90 ba...ko kuma zuwa lokacin da za a zaɓi sababbin shugabanni," a cewar sanarwar ta PDP.

A ƙarshen watan Nuwamba aka zaɓi sababbin shugabannin jam'iyyar na ƙasa, wadda a yanzu Kabiru Tanimu Turaki ke jagoranta a matsayin shugaba.

Post a Comment

Previous Post Next Post