Shawarwarin Dangote Ga Yan Najeriya Game Da Talauci

Attajirin nan na Afirka Aliko Dangote ya bai wa gwamnatin Najeriya da al'ummarta shawarwari kan yaƙi da talauci, bayan wata ganawa da ya yi da shugaban ƙasar Bola Tinubu a farkon wannan mako.

Daga alƙaluma na baya-baya da hukumar ƙididdiga ta Najeriya ta fitar, kimanin kashi 30.9% na al'ummar Najeriya ne ke rayuwa cikin ƙangin talauci, a cewar Bankin Duniya.

Hakan na nufin suna rayuwa a ƙasar da dalar Amurka 2.15 a kowace rana.

Bankin Duniya ya bayyana cewa gwamnati na buƙatar samar da sauye-sauyen da suka dace domin shawo kan matsalar talauci da ke ci gaba da yi wa al'umma katutu.

Rahoton Bankin ya ce duk da gwamnatin tarayyar ta ce ta fito da wasu shirye-shiryen, to amma ana tafiyar hawainiya wajen aiwatar da su.

Aliko Dangote, wanda ya fi kowa arziƙi a Afirka na da dukiyar da kimarta ta kai kimanin dala biliyan 30, bisa rahoton mujallar Forbes, inda ya tara arzikinsa ta hanyar manyan kamfanoninsa na siminti da sukari da takin zamani, sannan a baya-bayan nan katafariyar matatar man fetur.

Attajirin ya nuna damuwarsa kan yadda wasu masu kuɗi da manyan 'yan kasuwa ke rayuwa ba tare da la'akari da bukatun ƙasa ba.

Ya yi tsokaci kan yadda rayuwar alatu ke karkatar da hankali daga abin da zai kawo ci gaban tattalin arziki da ayyukan yi a ƙasa.

Post a Comment

Previous Post Next Post