ABBA ZAI YI DA-NA-SANIN BARIN NNPP: KWANKWASO

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa kuma jagoran jam'iyyar NNPP a Najeriya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya ce yana da yaƙinin cewa sai gwamnan Kano Abba Kabir da muƙarrabansa sun yi da na sanin fita daga jam'iyyar NNPP da suka yi.

Sanata Kwankwaso ya ce fitar gwamna Abba daga jam'iyyar NNPP ta zo da mamaki ga mutane da dama, kuma shi da kansa jin abin yake kamar a mafarki.

''Da yawa mutane ina da labarin, gani suke ma kamar wani tsari ne, da ni da shi, ko da ni da su. Nima sau da yawa ba na yarda cewar abubuwab da suke faruwa haka su ke.'' in ji Kwankwaso.

A ranar Litinin 26 ga watan Janairun 2026 gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya komawa jam'iyyar APC a hukumance, bayan sanar da ficewar sa daga NNPP a ranar Juma'a 23 ga watan Janairun 2023, ƙasa da shekara uku bayan cin zaɓen gwamnan Kano a cikin ta.

A wajen bikin komawarsa APC, gwamna Abba Kabir Yusuf ya ce ya ɗauki matakin sauya sheƙar bisa la'akari da inda aka dosa a siyasar Najeriya da kuma buƙatar bin hanyar da za ta kawo ci gaba ga jama'ar Kano baki ɗaya.

Ya kuma ce sai da ya yi tuntuɓa a tsakanin abokan tafiyar shi a siyasance da sauran masu ruwa da tsaki kafin yanke hukuncin sauya shekar.

Amma a hirar ta farko da kafafen yaɗa labarai tun bayan raba gari da gwamna Abba Kabir, Sanata Kwankwaso ya shaidawa BBC cewa akwai takaici yadda gwamna Abba Kabir ''ya ɗauki haƙƙin ƴan jam'iyar NNPP da kuma jama'ar Kano ya miƙa ga tafiyar Gandujiyya'' ba tare da wata ƙwaƙƙwarar hujja ba.

Sanata Kwankwaso ya ce ''Ni kaina in na kwanta sai in waiwaya in ce me ya faru? waye ya yi laifi? Ni ne na yi laifi? jam'iyya ce ta yi laifi? ƴan jam'iyya ne suka yi laifi? na kasa samun amsa.''

Ya kuma ce sai da ya yi tuntuɓa a tsakanin abokan tafiyar shi a siyasance da sauran masu ruwa da tsaki kafin yanke hukuncin sauya shekar.

Amma a hirar ta farko da kafafen yaɗa labarai tun bayan raba gari da gwamna Abba Kabir, Sanata Kwankwaso ya shaidawa BBC cewa akwai takaici yadda gwamna Abba Kabir ''ya ɗauki haƙƙin ƴan jam'iyar NNPP da kuma jama'ar Kano ya miƙa ga tafiyar Gandujiyya'' ba tare da wata ƙwaƙƙwarar hujja ba.

Sanata Kwankwaso ya ce ''Ni kaina in na kwanta sai in waiwaya in ce me ya faru? waye ya yi laifi? Ni ne na yi laifi? jam'iyya ce ta yi laifi? ƴan jam'iyya ne suka yi laifi? na kasa samun amsa.''

Post a Comment

Previous Post Next Post