Akwai Sauran Rina a Kaba a Matsalar Tsaro : CG Musa

Yayin da matsalar tsaro ta ƙi ci ta ƙi cinyewa a sassan Najeriya, ministan tsaron ƙasar, Janar Christopher Musa, ya ce gwamnati na bin tsarin da ya dace wajen magance matsalar, inda ta ke haɗa ayyukan soji da kuma sauran dabaru.

A wata hira da ya yi da BBC, Janar Musa mai ritaya ya amince cewa har yanzu akwai rina a kaba a yaƙin da gwamnatin ke yi da matsalar inda ya jaddada buƙatar tabbatar da tsaron kan iyakokin Najeriya don hana zirga-zirgar masu aikata laifuka.

Najeriya na fuskantar matsalar tsaro ta Boko Haram wadda ta shafe sama da shekara 15 tana fama da ita. Har yanzu ƙungiyar na da ƙarfin kai hare-hare nan da can, tare da hana manoma da masunta gudanar da ayyukansu.

Matsalar ƴan awaren Ipob, ita ma ta ƙi ci ta ƙi cinyewa, inda ƴan bindigan ke ƙaƙaba wa fararen hula dokoki da kuma ya wa mutane kisan ɗauki ɗaiɗai a kudu maso gabashin ƙasar.

A arewa ta tsakiyar ƙasar ana ci gaba da fuskantar daɗaɗɗiyar matsalar rikici tsakanin manoma da makiyaya waɗanda ke hanƙoron samun filayen gudanar da sana'o'insu.

Wata matsalar tsaro da ta ɓullo daga baya, wadda kuma ke addabar ƙasar ita ce ta ƴan bindiga masu kisa da satar mutane domin kuɗin fansa a arewa maso yammacin ƙasar; ta haifar da ɗimbin ƴan gudun hijira da kuma durƙusar da ayyukan tattalin arziƙi.

Wasu daga cikin matakan da gwamnatin Najeriyar ta ɗauka a yunkurin magance matsalar, sun hada da kafa sansanonin soji a irin waɗannan wuraren da ake fama da rashin tsaro da kuma sayo makamai daga ƙasashen ƙetare.

Sai dai duk da haka matsalar na ci gaba da addabar yankunan ƙasar.

mutane,'' in ji shi.

Post a Comment

Previous Post Next Post