Babu Sauran Kulawa da Gwamnati ke Bai wa Iyalin Tafawa Balewa'

Yayin da ake cika shekara 60 da juyin mulkin soji na farko a Najeriya, BBC ta kai ziyara inda aka binne gawar mutum mafi girman muƙami da aka kashe a lokacin juyin mulkin.

Abubakar Tafawa Ɓalewa shi ne Firaiministan Najeriya na wancan lokaci, kuma yana cikin waɗanda sojojin suka hallaka a shekarar 1966, baya ga Firimiyan jihar Arewa da na Yamma da kuma manyan sojoji da masu riƙe da muƙaman gwamnati.

Shi ne juyin mulkin da ya kawo ƙarshen jamhuriya ta farko a Najeriya, wadda ta ƙunshi fitattun mutane da suka yi fafutikar samun ƴancin kan ƙasar.

An binne marigayin ne a garin Bauchi da ke jiharsa ta asali a arewa maso gabashin Najeriya

Post a Comment

Previous Post Next Post