Lamarin ya samo asali ne tun bayan rahotannin da ke nuna cewa gwamnan jihar Abba Kabir ya sha alwashin sauya sheƙa zuwa jam'iyyar APC mai mulki a matakin tarayya.
Lamarin ya damalmala fagen siyasar Kano, inda mabiya suka faɗa cikin hali na rashin tabbas.
Abubuwan sun ci gaba da ɗaukar zafi har zuwa ranar Talata, inda jagoran jam'iyyar NNPP Rabi'u Kwankwaso - ubangidan siyasar Gwamna Abba Kabir - ya fitar da sanarwar cewa mabiyansa da ke cikin gwamnatin jihar na fuskantar matsin ɗaukar matsaya.
A wani bidiyo da ya wallafa a shafin facebook, Kwankwaso ya ya ce ''Gwamnati ta fito da wani tsari na takura wa ciyamomi da kansiloli da sakatarori da sauran masu riƙe da muƙami da nufin cewa su rubuta sunansu domin nuna, wa suke so, Kwankwasiyya suke so ko Gandujiyya.''