Hukumar kula da 'yan gudun hijirar Falasdinawa ta ce ginin shalkwatarta da ke Gabar yamma da kogin Jordan da aka fara rushewa yanzu yakama da wuta.
A makon daya gabata ne mahukuntan Isra'ila suka lalata wanu ɓangare na ginin hukumar.Cikin wata sanarwa da ya sanya a shafinsa na X, shugaban hukumar Philippe Lazzarini,ya ce wutar da aka sanyawa ginin na su a yanzu shi ne hari na baya bayan nan da aka kai musu a wani yunƙuri na tarwatsa hukumar.
Ba dai a bayar da cikakken bayani akan yadda wutar ta tashi a ofoshin hukumar ba.