Trump ya ce: Amurka za ta jagoranci Venezuela har zuwa lokacin kafa gwamnati

Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce ƙasarsa za ta ja ragamar gwamnatin Venezuela har zuwa lokacin da al'amura za su daidaita tare da miƙa mulki ga gwamnatin da za a kafa.

Da safiyar yau Asabar ne Trump ya sanar da kama shugaban Venezuela Nicolas Maduro da mai ɗakinsa a wani ''mummunan'' hari da Amurka ta kai ƙasar.

Kawo yanzu dai bayanai na cewa Mista Maduro na New York inda zai fuskanci shari'a kan zargen-zargen safarar miyagun ƙwayoyi.

Post a Comment

Previous Post Next Post