Yanbindiga Sun yi Garkuwa da Mutane 26 a Talatar Mafara

Hukumomi a jihar Zamfara, mai fama da matsalar tsaro a arewa maso yammacin Najeriya sun tabbatar da sace mutane 26 a wasu hare-hare da ƴan bindiga suka kai kan ƙauyuka biyu na ƙaramar hukumar Talatar Mafara a ƙarshen mako.

Talatar Mafara na daga cikin ƙananan hukumomin da ke fama da matsalar tsaro a jihar, inda a shekarar 2021 ƴan bindiga suka sace ɗaliban makarantar mata ta Jangebe, kimanin 300.

A tattaunawa da BBC, shugaban ƙaramar hukumar Talatar Mafara Yahaya Yari Abubakar ya ce ƴan bindigar sun kai hare-hare biyu a cikin ƙarshen mako.

"Shekaran jiya an shiga wani ƙauye mai suna Matuna, inda suka ɗauki mutum uku suka kuma kashe mutum ɗaya," a cewar Yari Abubakar.

Ya ƙara da cewa "sai suka sake dawowa suka sake kai hari a wani ƙauye da ake ce wa Tashar Kuturu, suka ɗauki mutum 23 kuma suka harbi wani mutum a hannu da kafa, mun kai shi asibitin cikin garin Jangebe ana nema masa lafiya."

A ranar Litinin ne rahotanni suka ɓulla kan cewa wasu ƴan bindiga sun kai hari tare da sace mutane da dama waɗanda aba a ƙididdige yawansu ba.

A baya-bayan nan ƴan bindiga sun matsa ƙaimi wajen kai hare-hare a jihohin arewa maso yammacin Najeriya, inda suka kashewa da kuma sace mutane domin karɓar kuɗin fansa.

A makon da ya gabata wasu ƴan bindiga sun kai hari a Kajuru da ke jihar Kaduna inda suka sace masu ibada kimanin 170 a ƙauyen Kurmin Wali, inda duk da cewa wasu sun tsero, amma har yanzu akwai mutum 160 wadanda ba a san halin da suke ciki ba.

Haka nan a baya-bayan nan mahara sun kai hari a Makarantar Sakandiren Ƴanmata da ke garin Maga a jihar Kebbi, inda suka kashe mai gadi da sace ɗalibai 25.

Jim kaɗan bayan haka wasu ƴan bindigan sun kai hari a wata makaranta da ke ƙauyen Papiri a jihar Neja inda suka sace ɗalibai da malamai kusan 200.

Hukumomi a Najeriya na cewa suna ƙoƙari wajen magance matsalar, sai dai har yanzu ƴan bindigar na ci gaba da kai irin wadannan hare-hare waɗanda ke janyo salwantar rayuka da dukiya.

Lamarin ya haifar da durkushewar ayyukan tattalin arziki a yankin, inda manoma da dama ke gudun hijira, wasu kuma ba su iya noma kamar yadda suka saba yi a baya.

Post a Comment

Previous Post Next Post