Yara 100 sun mutu a Gaza tun bayan tsagaita wuta - MDD

Majalisar Dinkin Duniya ta ce aƙalla yara 100 sojojin Isra'ila suka kashe a Gaza tun bayan tsagaita wutar da aka yi watanni uku da suka gabata.

Asusun kula da ƙananan yara na majalisar, UNICEF, ya ce a ƙiyasi duk rana ɗaya sojojin Isra'ila ko hare- harensu ta sama na kashe yaro ɗaya.

Wani mai magana da yawun hukumar ya ce duk da dai yarjejeniyar ta rage yawan hare- haren, hakan bai wadatar ba saboda har yanzu ana binne yara.

Majalisar Dinkin Duniyar ta kuma ce aƙalla yara shida ne suka mutu a Gaza a makonni biyu da suka gabata saboda yanayi na tsananin sanyi.

Post a Comment

Previous Post Next Post