Shin Akwai Zaluncin Da Ya Kai Adalcin Mu'utazilawa Girman Zalunci?

Rukuni na biyu a cikin rukunai biyar na Mu'utazilanci shi ne Adalci.

To miye ma'anar adalci a wajen Mu'utazilawa?

Ga nan bujumin Malami a cikinsu, zai ba mu amsa inda ya ce:

"فإن قيل: فأخبرني عن العدل ما هو؟

قيل له: هو العلم بتنزيه الله عز وجل عن كل قبيح، وأن أفعاله كلها حسنة.

وتفسير ذلك؛ أن تعلم أن جميع أفعال العباد من الظلم والجور وغيرهما لا يجوز أن يكون من خلقه. ومن أضاف ذلك إليه فقد نسب إليه الظلم والسفه، وخرج من القول بالعدل...

وتعلم تعالى أنه لا يريد المعاصي ولا يشاؤها...".

الأصول الخمسة للقاضي عبد الجبار المعتزلي (ص: ٦٩)

Ka ga ƙarara, a fili, Babban Malamin Mu'utazilawan ya ce: ma'anar Adalcin Allah shi ne; a tsarkake Allah daga munanan abubuwa. Fassarar haka shi ne:

"Ka san cewa; dukkan aiyukan bayi na zalunci da danne haƙƙi da wasunsu, bai halasta su kasance halittar Allah ba. Duk wanda ya danganta halittarsu ga Allah to ya danganta masa zalunci da wauta (rashin hikima), ya fita daga Aƙidar Adalci...

Kuma ka san cewa; Allah Maɗaukaki ba ya nufin faruwar aiyukan saɓo, kuma ba ya ganin daman faruwarsu...".

Wannan shi ne ra'ayinsu.

Alhali Allah ya ce:

﴿وَٱللَّهُ خَلَقَكُمۡ وَمَا تَعۡمَلُونَ ۝٩٦﴾ [الصافات ٩٦]

{Kuma Allah ne ya halicce ku, da ma abin da kuke aikatawa}.

Kuma ya ce:

﴿وَمَا تَشَاۤءُونَ إِلَّاۤ أَن یَشَاۤءَ ٱللَّهُۚ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ عَلِیمًا حَكِیمࣰا﴾ [الإنسان ٣٠]

{Kuma ba za ku ga daman aikata wani abu ba, sai idan Allah ya ga dama}.

To ka ga wannan ra'ayi nasu, ya ci karo da Alƙur'ani da Sunna. Da ma su ba ruwansu da Alƙur'ani, balle Hadisi a wannan babin. Sai dai hankalinsu (son zuciyoyinsu) kawai.

Don haka, idan ka san haƙiƙanin zalunci a Shari'a, to lallai za ka san cewa; Adalcin Mu'utazilawa na cewa; Allah bai halicci aiyukan bayi ba, kuma bai ƙaddara su ba, - wai - bayi ne suka halicci aiyukansu da kansu, wannan shi ne zalunci mafi girma. Saboda zalunci nau'i uku ne:

1- Shirka ma Allah.

2- Zaluntar bawa, da danne masa hakki.

3 - Zaluntar kai, ta hanyar aikata saɓo.

A cikinsu, na farkon - wato shirka ma Allah - shi ne zalunci mafi girma.

﴿إِنَّ ٱلشِّرۡكَ لَظُلۡمٌ عَظِیمࣱ﴾ [لقمان ١٣]

{Lallai shirka zalunci ne mai girma}

To bisa wannan Adalci nasu, Mu'utazilawa shirka suke yi ma Allah, shirkan ma mafi munin shirka, wato shirka ma Allah a cikin Rububiyya da halitta.

To idan Adalcin Mu'utazilawa shi ne cewa; Allah bai halicci aikin bawa ba, bawa shi ya halicci aikinsa, to wannan sanya ma Allah abokin tarayya ne a halitta. Wannan kuwa shirka ne a Rububiyya. Ma'ana; Allah ba shi kaɗai ne mahalicci ba, kowane bawa ma mahalicci ne, shi ne mahaliccin aiyukansa, shi yake halittarsu da kansa.

To ka ga a fili; wannan shirka ne ma Allah! Kai, shi ne ma shirka mafi girma kai tsaye, wato shirka a cikin Rububiyya, shirkan da hatta Mushrikan Makka ba su yi irinsa ba.

Saboda haka Adalcin Mu'utazilawa babu abin da zai koyar da kai sai zalunci, zaluncin ma mafi girman zalunci.

Don haka duk mai son koyon adalci, to ya koma ga Littafin Allah, da Sunnar Manzonsa (saw), da Tarihin Khalifofinsa da Sahabbansa. Ba a ce; mutum ya koma adalcin Mu'utazilawa ba, wanda shi ne ƙololuwar zalunci a bayan ƙasa.

To yanzu, don Allah, wannan adalcin ne ake so a tallata shi wa mutane?!

Tir!

***

Hadisan Annabi (saw) su ne Ma'auni

Yarda da Hadisan Annabi (saw) da binsu, shi ya banbance tsakanin Ahlus Sunna da ƴan bidi'a.

Zai yi wahala ka samu mutum mai amsa sunan Musulmi, amma kuma ya ce maka bai yarda da Alƙur'ani (a dunƙule) ba.

Amma za ka samu da yawa suna inkarin Hadisai. Imma inkarin Hadisan duka gaba ɗaya, ko ɓangare. Musamman Hadisan Aƙida, ko Hadisan da suka shafi rayuwar Annabi (saw), da zamantakewarsa.

Wannan ya sa, Alamar ɗan bidi'a ita ce ƙin Hadisan Annabi (saw).

Saboda duk wani ɗan bidi'a za ka same shi yana ƙin wasu Hadisai, yana sukarsu, ko yana ƙaryata su.

Waɗanne Hadisai ne haka?

Su ne Hadisan da suka saɓa son zuciyarsa,

Hadisan da suka saɓa bidi'arsa,

suka saɓa ra'ayoyin shehinsa,

ko ra'ayoyin ƙungiyarsa.

Amma da zaran ka ga mutum ya yarda da Hadisan Annabi (saw), ingantattu, to wannan shi ne Ahlus Sunna.

Don haka alamar Ahlus Sunna ita ce bin Hadisan Annabi (saw).

Alamar ƴan bidi'a kuma kishiyar haka.

Mai hankali shi ne wanda ya dauki Duniya a matsayin gada da zai hau ya tsallaka zuwa ga rayuwa matabbaciya. Allah ya ba mu labarin wani mai hankali yana wa'azi ga mutanensa inda ya ce:

{يَاقَوْمِ إِنَّمَا هَذِهِ الْحَيَاةُ الدُّنْيَا مَتَاعٌ وَإِنَّ الْآخِرَةَ هِيَ دَارُ الْقَرَارِ} [غافر: 39]

"Ya ku mutane na, lallai ku sani, wannar rayuwar Duniyar fa dan jin dadi ne kadan, Lahira fa ita ce digan tabbata".

Kowa yana ganin abin da yake faruwa, Duniya za ta yi dadi ta yi kyau, ta zama abin sha'awa a idon mai kallonta, sai ya karkata gare ta, ya manta da hikimar halittarsa, ya mayar da manufar rayuwarsa ita ce samun abin Duniya da jin dadi da sharholiya a cikinta, sai ta gama jan hankalinsa, ya gama ruduwa da ita, har sai ya yi zaton ya same ta, yana ganin ya gama mallakarta, kawai sai ya ji gyat, mai yanke jin dadi ta yanke masa jin dadin Duniya, shi kenan kuma an rabu.

Ya kamata ka zama mai hankali, rayuwa da mutuwa duka masu wa'azi ne.

Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani

zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani

Abu-Ubaida Sani

I provide language services such as translation, transcription, proofreading, interpretation, etc in the Hausa language. I also outsource in Pidgin, Yoruba, Igbo, Fulah, and Kanuri. Contact me through email: abuubaidasani5@gmail.com or WhatsApp: +2348133529736

Post a Comment

Previous Post Next Post