Za mu Kawar da Barazanar Yanbindiga a Najeriya - Tinubu

Shugaban majalisar malamai na ƙungiyar Izalatil Bid’ah Wa’ikamatis Sunnah (JIBWIS), Sheikh Sani Yahaya Jingir, ya bayyana kasancewar Farfesa Joash Ojo Amupitan a matsayin shugaban hukumar zaɓen Najeriya matsayin kasada.

Yayin da yake jawabi a ƙarshen bitar kwana uku da ƙungiyar Izala ta shirya a a birnin Jos, Sheikh Jingir ya ce Musulman Najeriya ba su amince da naɗin Amupitan a atsayin shugaban INEC ba, kamar yadda Jardiar Daily Trust ta ruwaito.

Amupitan na fsuaknatr suka tsakanin Musulman ƙasar kan wata takarda da ya rubuta shekarun baya kan ƙorafin kisan ƙare dangin da ake yi wa Kiristocin ƙasar.

Sheikh Jingir ya ce shugaban INEC ya taɓa zargin Musulmai da kisan ƙare dangi a kan Kiristoci a fili, don haka bai kamata a ba shi muƙamin da ya shafi muhimman ayyuka kamar na INEC ba.

“Me yasa mutumin da ya zagi Sheikh Usman Danfodio da Musulmai a kuma naɗa shi shugaban INEC?” in ji Sheikh Jingir.

Sheikh Jingir ya yi mamakin shiru da ‘yan Majalisar Dokoki suka yi kan wannan al’amari, inda ya yi kira su tabbatar an yi adalci wajen naɗin shugaba mai gaskiya ga hukumar.

A baya-bayan nan ma Majalisar Ƙoli kan harkokin Addinin Musulunci a Najeriya ta yi kiran cire shugaban na INEC saboda wannan zargi.

Duk da gwamnatin Tinubu ta musanta zargin kisan kiristoci a ƙasar, har yanzu ba ta mayar da martani kan kiran cire Amupitan daga muƙamin ba.

Post a Comment

Previous Post Next Post