Shigar Malamai Siyasa Yana Kawo Muhawara a Arewacin Najeriya

Ana muhawara a Najeriya musamman a shafukan sada zumunta bayan da fitaccen malamin Addinin Musulunci, kuma tsohon ministan sadarwa Sheikh Ali Pantami ya sake motsa siyasarsa.

A ƙarshen makon da ya gabata ne malamin ya je harabar sakatariyar jam'iyyar APC ta jihar Gombe inda ya sabunta rajistarsa.

Tsohon ministan sadarwar ya kuma zagaya sassan birnin Gombe bisa rakiyar dubban magoya bayansa.

Wannan ba shi ne karon farko da shigar malaman Addinin Musulunci harkar siyasa ya janyo muhawara a tsakanin al'umma ba.

Rawar da tsohon ɗan takarar gwamnan jihar Kano Sheikh Ibrahim Khalil ke takawa a fagen siyasar jihar abu ne da ya daɗe yana haifar da muhawara.

Haka nan ma a lokuta da dama akan tsangwami malaman addinin Musulunci da ke tattaunawa kan lamuran siyasa a lokutan wa'azi ku huɗubobi, inda ake ganin tamkar 'suna shiga wani fage da ba nasu ba'.

Duk da kasancewarsa Ali Pantami tsohon minista a gwamnatin Muhammadu Buhari, da dama ƴan ƙasar ba sa yi masa kallon ɗansiyasa, a maimakon haka suna ganin Buhari ya naɗa shi muƙamin ne domin ƙwarewarsa a fannin sadarwa.

Post a Comment

Previous Post Next Post