Mitoci kaɗan ne tsakanin tsohon garin Dubai da kuma magudanar ruwan da ta raba tsakiyar birnin. Hayaƙi ya turnuƙe sararin samaniya a daren Talata 3 ga watan Maris.
Kamar yadda gwamnatin Haɗaɗɗiyar Daular Larabawan ta tabbatar, wani harin jirgi maras matuƙi ya sauka a birnin bayan yaƙin da aka fara tsakanin Iran da Isra'ila da Amurka.Sabon harin ya farmaki ofishin jakadancin Amurka ne, kuma ya sauka a kan wajen ajiye motoci amma babu wanda ya raunata.
A wani harin da Iran ta kai kafin wannan ma, jirgi maras matuƙi ya kai hari kan ofishin jakadancin Amurka da ke Riyadh a Saudiyya.
Waɗannan misalin su ne na baya-bayan nan a rikicin da ake yi, wanda aka fara tun bayan kisan Ayatollah Ali Khamenei.
Waɗannan hare-haren na matuƙar tasiri a ƙasashen yankin Gulf ko kuma a ce ƙasashen Larabawa, irinsu Dubai da Qatar da Bahrain da Kuwait da Oman da Saudiyya.
Iran ta bayyana cewa ta kai harin ne kan sansanonin Amurka a waɗannan ƙasashen, amma kuma tarkacen makamai masu linzamin da na jirage marasa matuka sun riga sauka a kan wasu otel-otel da filayen jiragen sama a yankin.
Har yanzu babu tabbacin ko da gangan Iran ta kai hari wajen shaƙatawa da wasu muhimman wurare ko kuma kawai tsautsayi ne ya faɗa kansu a lokacin da take ƙoƙarn kai harin a Amurka, kamar yadda Farfesa Daniel Rio Tinto, ƙwararre a fannin tsaron ƙasa da ƙasa ya yi hasashe.