Me ya sa Iran ke kai wa Kasashen Musulmi da ke Makwaftaka da ita Hari?

Mitoci kaɗan ne tsakanin tsohon garin Dubai da kuma magudanar ruwan da ta raba tsakiyar birnin. Hayaƙi ya turnuƙe sararin samaniya a daren Talata 3 ga watan Maris.

Kamar yadda gwamnatin Haɗaɗɗiyar Daular Larabawan ta tabbatar, wani harin jirgi maras matuƙi ya sauka a birnin bayan yaƙin da aka fara tsakanin Iran da Isra'ila da Amurka.

Sabon harin ya farmaki ofishin jakadancin Amurka ne, kuma ya sauka a kan wajen ajiye motoci amma babu wanda ya raunata.

A wani harin da Iran ta kai kafin wannan ma, jirgi maras matuƙi ya kai hari kan ofishin jakadancin Amurka da ke Riyadh a Saudiyya.

Waɗannan misalin su ne na baya-bayan nan a rikicin da ake yi, wanda aka fara tun bayan kisan Ayatollah Ali Khamenei.

Waɗannan hare-haren na matuƙar tasiri a ƙasashen yankin Gulf ko kuma a ce ƙasashen Larabawa, irinsu Dubai da Qatar da Bahrain da Kuwait da Oman da Saudiyya.

Iran ta bayyana cewa ta kai harin ne kan sansanonin Amurka a waɗannan ƙasashen, amma kuma tarkacen makamai masu linzamin da na jirage marasa matuka sun riga sauka a kan wasu otel-otel da filayen jiragen sama a yankin.

Har yanzu babu tabbacin ko da gangan Iran ta kai hari wajen shaƙatawa da wasu muhimman wurare ko kuma kawai tsautsayi ne ya faɗa kansu a lokacin da take ƙoƙarn kai harin a Amurka, kamar yadda Farfesa Daniel Rio Tinto, ƙwararre a fannin tsaron ƙasa da ƙasa ya yi hasashe.

Post a Comment

Previous Post Next Post