Wane ne Mojtaba Khamenei, Wanda ake hHasashen Zai Zama Jagoran Addinin Iran?

Bayan kashe jagoran addinin Iran, Ali Khamenei a hare-haren Amurka da Isra'ila a Iran, sai aka fara tunanin ko ɗan marigayin Mojtaba wanda shi ma yake da ƙarfin faɗa a ji ya rasu.

Khumain
Sai da aka yi kwanaki ba a ji ɗuriyarsa ba, kuma babu tabbaci. Sai a ranar Talata 3 ga watan Maris ne kafofin watsa labarai suka tabbatar da cewa Mojtaba yana raye, kuma yana cikin ƙoshin lafiya. Sai dai har yanzu bai fito ba.

Yanzu yana cikin na gaba-gaba a cikin waɗanda ake hasashen za su iya maye gurbin jagoran addinin ƙasar, kamar yadda kafar Reuters ta ruwaito daga wasu majiyoyi guda biyu a Iran.

Bayan haka, majalisar ƙwararru mai mambobi 88, wadda ke da alhakin naɗa sabon jagoran addinin ana cewa ta yi nisa a aikin naɗin sabon jagoran, duk da cewa zai yi wahala a sanar da sabon jagoran kafin a yi jana'izar marigayin.

Mojtaba, ba kamar mahaifinsa ba ne, domin ba a san shi sosai ba, kuma bai taɓa riƙe wani muƙamin gwamnati ba, sannan bai taɓa zantawa da menama labarai ba ballanta jawabi a wajen taro. Haka kuma tsirarun hotunansa da bidiyo ne kawai aka gani.

Post a Comment

Previous Post Next Post