Yadda aka kashe Kacalla Alti, Danbindigan da ke Dasa bama-bamai‘ a Zamfara

Gwamnatin jihar Katsina ta tabbatar da cewa sojojin Najeriya sun kashe ƴanbindiga 45 da suka kai hari wani ƙauye a jihar Katsina da ke arewacin ƙasar.

Kwamishinan tsaro da al'amuran cikin gida na jihar Katsina, Hon. Nasiru Mu'azu ya shaida wa BBC cewa cikin ƴanbindigar da aka kashe har da wasu manyan kwamadandojin ƴanbindiga biyu da suka addabi wasu yankunan jihohin Katsina da Zamfara, wato Kacalla Alti da Kacalla Damale waɗanda dukkansu yan'uwan juna ne.

Lamarin ya faru ne ranar Juma'a da maraice kamar yadda hukumomin jihar suka tabbatar.

Rahotonni sun ce tun da farko ƴanbindigar waɗanda suka taso daga jihar Zamfara mai makwabtaka, sun kai hari ƙauyen Alhazawa na ƙaramar hukumar Danmusa a ranar Alhamis domin satar shanu.

Post a Comment

Previous Post Next Post