Adadin mutanen da aka tabbatar sun kamu da cutar Ebola a Democratic Republic of the Congo ya kusan ninkuwa cikin ‘yan kwanaki kaɗan, yayin da shugaban World Health Organization (WHO), Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya kai ziyara yankunan da cutar ta fi kamari.
Rahotanni sun nuna cewa sabuwar ɓarkewar cutar Ebola mai nau’in Bundibugyo na ci gaba da yaɗuwa cikin sauri a gabashin DR Congo, musamman a lardin Ituri, inda jami’an lafiya ke fuskantar matsalolin tsaro da ƙarancin kayan aiki.
A cewar hukumomin lafiya, adadin waɗanda ake zargi sun kamu da cutar ya haura 1,000, yayin da tabbatattun masu ɗauke da cutar suka ƙaru sosai cikin kwanaki kaɗan da suka gabata.
Shugaban WHO ya yi kira ga al’ummomin yankin da su nemi magani da wuri tare da bin ƙa’idojin binne gawa cikin tsaro domin rage yaɗuwar cutar. Ya kuma bayyana cewa wannan nau’in Ebola ba shi da cikakkiyar rigakafi ko magani da aka amince da shi a yanzu.
Masana lafiya sun ce rikicin makamai, ƙaura da rashin tsaro na hana jami’an lafiya kaiwa yankunan da abin ya shafa cikin sauƙi. Haka kuma, an samu hare-hare kan cibiyoyin jinya da ma’aikatan lafiya daga wasu al’ummomi da ke adawa da matakan kariya da aka kafa.
Ƙasashe makwabta kamar Uganda sun riga sun tabbatar da wasu masu ɗauke da cutar, abin da ya ƙara tayar da hankalin duniya kan yiwuwar yaɗuwar Ebola zuwa wasu yankuna.
WHO ta yi kira ga ƙasashen duniya da su ƙara tallafin kuɗi da kayan agaji domin taimakawa wajen dakile cutar kafin lamarin ya ƙara taɓarɓarewa.