Ta shaida mana cewa jim kaɗan bayan rasuwar mijinta, ƴan bindigar da suka yi garkuwa da su sun shiga cikin tsananin tashin hankali da firgici.
Ba da jimawa ba suka kawo babura suka fara shirye-shiryen gaggawar tserewa. Suka ɗora ta a kan ɗaya daga cikin baburan sannan suka fice daga wurin da suke tsare da ita da mijinta tare da wasu a cikin ayari. Daga dukkan alamu, sun fi nuna sha'awa a kanta fiye da sauran waɗanda suka yi garkuwa da su, domin ba su yi wani yunƙuri na kwashe sauran mutanen ba.
A cewarta, yayin da ƴan bindigar ke gudu cikin daji a kan baburansu domin kauce wa arangama da sojoji, sai suka fara jin karar harbe-harbe daga nesa.
Ta ce wannan lamarin ya haddasa ruɗani a tsakaninsu, inda suka watse kowa ya kama gabansa maimakon su ci gaba da tafiya tare.
“Har ila yau, ta ce mutumin da ke ɗauke da ita a kan baburinsa ya fusata kuma ya tsaya a hanya. Ya tilasta mata sauka daga baburin sannan, mai yiwuwa saboda takaici, ya harbe ta a cinyarta kafin ya tsere.”
Majiyar ta ce matar Janar ɗin ta zubar da jini sosai yayin da take fama da matsanancin ciwo.
Ba za ta iya tsayawa ko tafiya ba saboda raunin harbin bindigar. A cikin wannan hali ne wani mutum daga wani ƙauyen kusa ya zo inda take,” in ji majiyar, bisa abin da ta ba su labari.
Ya ƙara da cewa:
A cewar Hajiya Amina, mutumin ya tambaye ta abin da ya faru, sai ta ba shi labarin halin da ta shiga. A lokacin tana cikin tsananin tsoro, tana haki kuma gumi na keto mata sosai.
Sai mutumin ya tambaye ta, ‘Ke ce matar Janar Rabe?’ Ta amsa masa da eh.
Ta ce yayin da mutumin ke ƙoƙarin taimaka mata, sai suka ji karar harbe-harbe, wanda ake kyautata zaton daga sojojin da ke tahowa suna binciken yankin domin neman ta.
Saboda haka, mutumin ya gudu domin tsira da ransa. Ta ce cikin ƴan mintuna kaɗan sojoji suka isa wurin suka same ta kwance cikin jini,” in ji majiyar.
Majiyar ta ce nan take wurin ya koma na murna bayan sojojin sun gano cewa matar Janar Rabe ce.
Ta ƙara cewa Hajiya Amina ta shaida musu cewa a lokacin ne mutumin da ya fara gano ta ya dawo wurin.
An gaya mana cewa sojojin ba su da wani abu a tare da su sai bindigoginsu, don haka suka roƙi mutumin ya kawo wani katako. Daga nan suka ɗora matar Janar a kai suka kai ta zuwa motarsu, sannan suka garzaya da ita wani asibiti a wani gari makwabta, inda aka ba ta agajin gaggawa kafin daga bisani aka mayar da ita zuwa Asibitin Koyarwa na Tarayya (FMC) da ke Katsina,” in ji shi.
An kuma bayyana cewa harbin da ya samu Hajiya Amina bai kai ga barazana ga rayuwarta ba, domin harsashin bai karya ƙashin cinyarta ba.
Harsashin ya huda naman saman ƙafarta tsakanin ƙugu da gwiwa. Amma da hakan ma na iya zama sanadin mutuwarta saboda yawan jinin da take zubarwa,” in ji majiyar.
(Majiyar Labari: Daily Trust)
