Shugaban Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na ƙasa, Nentawe Yilwatda, ya bayyana cewa sake zaɓen Gwamna Biodun Oyebanji a Jihar Ekiti State da kuma gagarumar nasarar jam’iyyar a zaɓukan cike gurbi daban-daban a faɗin ƙasar alama ce ta amincewar jama’a ga APC da kuma manufofin sauye-sauyen Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara kan yaɗa labarai, Abimbola Tooki, ya fitar, Yilwatda ya ce sakamakon zaɓen ya nuna cewa ‘yan Najeriya na yaba da shugabanci nagari, ci gaba da ayyukan raya ƙasa, da kuma fa’idojin sauye-sauyen tattalin arziki da ake aiwatarwa.
Ya ce nasarar Gwamna Oyebanji ta nuna cewa aiki da sakamako su ne mafi ƙarfi a siyasar dimokiraɗiyya, yana mai ambaton nasarorin da aka samu a fannonin gine-gine, lafiya, ilimi, noma, ƙarfafa matasa da jin daɗin ma’aikata.
Shugaban APC ɗin ya ƙara da cewa nasarar jam’iyyar a Ekiti da kuma a biyar daga cikin zaɓukan cike gurbi shida da aka gudanar a faɗin ƙasa na nuna goyon bayan jama’a ga manufofin APC na shugabanci da ci gaba.
Ya kuma danganta wannan nasara da ƙara samun amincewar jama’a ga shirin sauye-sauyen Shugaba Tinubu, yana mai cewa yana kafa tubalin tattalin arziki mai ƙarfi da ɗorewa a Najeriya.
Yilwatda ya taya Shugaba Tinubu, Gwamna Oyebanji, ‘yan APC da dukkan waɗanda suka yi nasara murna, tare da yaba wa hukumar zaɓe ta INEC, jami’an tsaro da mutanen Ekiti saboda gudanar da zaɓe cikin lumana.
Ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa APC za ta ci gaba da jajircewa wajen samar da shugabanci nagari, farfaɗo da tattalin arziki da kuma ci gaban ƙasa mai ɗorewa ga kowa.