Yan Bindiga sun kashe Manoma a Sakkwato

Aƙalla manoma 14 ne suka rasa rayukansu bayan da wasu 'yan bindiga suka kai hare-hare a garuruwa kusan bakwai da ke ƙananan hukumomin Isa da Sabon Birni a jihar Sakkwato.

Rahotanni sun ce maharan sun farmaki manoman ne yayin da suke gudanar da ayyukan noma a gonakinsu, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutanen tare da haddasa fargaba a tsakanin al'ummomin yankin.

Honarabul Muhammad Sa'idu Bargaja, mai wakiltar mazabar Isa da Sabon Birni a majalisar wakilan kasar, ya shaida wa BBC cewa barayin sun daidaici lokacin da aka samu ruwa yayin da manoma ke fitowa gonakinsu don yin shuga, inda suke amfani da wannan dama wajen aiwatar da manufarsu.

''Wannan al'amari ya faru ne a yammacin Isa, da Tidibale, da Mansalawa, da Tsabare, da Hadawa, da Masawa, Gidan Nagora,

Ya ce baya ga wadanda aka kashe akwai kuma mutane da dama da yanzu haka ke cikin daji bayan yan bindigar sun yi awon gaba da su.

Dan majalisar ya shaida wa BBC cewa ko a makon da ya gabata sai da yan fashin suka kai wa mutane hari tare da kashe kimanin mutum bakwai a wurare daban-daban.

Post a Comment

Previous Post Next Post